Fasaha Stream
LIVE Radio
Fasaha Stream
LIVE Radio

Hajjin 2026: Mahajjatan Katsina za su biya Naira Miliyan 7.67 bayan an rage farashin kujeru

-

Katsina, Lahadi, 10 ga Nuwamba, 2025

An rage kudin kujerar aikin Hajjin 2026 ga mahajjatan Jihar Katsina da sauran jihohin Arewacin Najeriya zuwa Naira Miliyan 7.67, bisa sabuwar sanarwar Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON).

Shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya bayyana hakan cikin wata hira da DCL Hausa daga kasar Saudiyya, inda ya ce rage kudin ya zama dole ne bayan amincewar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da bayar da tallafi don rage nauyin kudi ga masu niyyar zuwa hajji.

Farfesa Pakistan ya ce, hakan kuma ya biyo bayan tattaunawa ta baya-bayan nan da hukumar ta yi da kamfanonin masu samar da hidimomi daga Saudiyya.

A karkashin sabon tsari, jihohin da ke yankin Borno da Adamawa za su biya Naira 7,579,020, yayin da mahajjatan Katsina da sauran jihohin Arewa za su biya Naira 7,669,769. Daga bangaren jihohin Kudu kuwa, za su biya Naira 7,991,141, sabanin Naira 8,784,085 da aka sanar a baya.

Shugaban NAHCON ya ce wannan ragin kudin ya nuna kokarin gwamnati na saukaka wa alhazai domin karin halarta a aikin Hajjin bana.

A karshe, hukumar ta kayyade ranar 5 ga watan Disamba, 2025, a matsayin ranar karshe ta biyan kuɗin Hajji ga duk masu niyyar tafiya. NAHCON ta shawarci masu niyyar zuwa su kammala biyan kuɗinsu kafin wannan lokaci domin tabbatar da samun kujerarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

FG Launches School Safety Policy in Katsina to Tackle Violence, Insecurity

KATSINA — The Federal Government has launched the Katsina State Policy on Safety, Security, and Violence-Free Schools, aimed at protecting students from insecurity and ensuring...

Katsina Begins Fertiliser Distribution in Charanci, Warns Against Price Hike

KATSINA — The Katsina State Government has commenced the distribution of subsidised fertiliser to farmers, with strict warnings against price inflation beyond the approved rate...

NGF Chairman, Education Minister Commission Radda Model Secondary School in Katsina

KATSINA — Chairman of the Nigerian Governors’ Forum and Governor of Kwara State, Abdulrahman Abdulrazaq, has commissioned the multi-million naira Radda Model Secondary School in...

Most Popular