Fasaha Stream
LIVE Radio
Fasaha Stream
LIVE Radio

Hajjin 2026: Mahajjatan Katsina za su biya Naira Miliyan 7.67 bayan an rage farashin kujeru

-

Katsina, Lahadi, 10 ga Nuwamba, 2025

An rage kudin kujerar aikin Hajjin 2026 ga mahajjatan Jihar Katsina da sauran jihohin Arewacin Najeriya zuwa Naira Miliyan 7.67, bisa sabuwar sanarwar Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON).

Shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya bayyana hakan cikin wata hira da DCL Hausa daga kasar Saudiyya, inda ya ce rage kudin ya zama dole ne bayan amincewar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da bayar da tallafi don rage nauyin kudi ga masu niyyar zuwa hajji.

Farfesa Pakistan ya ce, hakan kuma ya biyo bayan tattaunawa ta baya-bayan nan da hukumar ta yi da kamfanonin masu samar da hidimomi daga Saudiyya.

A karkashin sabon tsari, jihohin da ke yankin Borno da Adamawa za su biya Naira 7,579,020, yayin da mahajjatan Katsina da sauran jihohin Arewa za su biya Naira 7,669,769. Daga bangaren jihohin Kudu kuwa, za su biya Naira 7,991,141, sabanin Naira 8,784,085 da aka sanar a baya.

Shugaban NAHCON ya ce wannan ragin kudin ya nuna kokarin gwamnati na saukaka wa alhazai domin karin halarta a aikin Hajjin bana.

A karshe, hukumar ta kayyade ranar 5 ga watan Disamba, 2025, a matsayin ranar karshe ta biyan kuɗin Hajji ga duk masu niyyar tafiya. NAHCON ta shawarci masu niyyar zuwa su kammala biyan kuɗinsu kafin wannan lokaci domin tabbatar da samun kujerarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Begins Selection of 34 Students for MBBS Scholarships in Russian Universities

The Katsina State Government has commenced the selection process for a special foreign scholarship programme that will sponsor 34 indigenous students to study Medicine (MBBS)...

FG Launches FreeTV Platform, Offers Nigerians Over 100 Subscription-Free Channels

The Federal Government has officially launched the FreeTV Direct-to-Home (DTH) platform, marking a major milestone in Nigeria's long-delayed Digital Switch-Over (DSO) programme and paving the...

Housing Minister Darma Inspects Digital Land Platform Ahead of Launch, Reaffirms Commitment to Modernising Land Administration

ABUJA — Minister of Housing and Urban Development, Engr. Muttaqha Rabe Darma, has inspected the Centralised Land Repository and Management System (CLRMS) ahead of its...

Most Popular