Fasaha Stream
LIVE Radio
Fasaha Stream
LIVE Radio

Zuri’ar Danwaire Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Mai Martaba Sarkin Katsina Kan Rasuwar Sarkin Ruma

-

Daga Sada Rumah

Zuri’ar Danwaire daga Karamar Hukumar Batsari sun kai ziyarar ta’aziyya ga Mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji (Dr.) Abdulmumin Kabir Usman, kan rasuwar marigayi Sarkin Ruma, Hakimin Batsari.

Ziyarar, wadda aka kai yau a Fadar Sarkin Katsina, ta kasance ne domin jajantawa Mai Martaba bisa rasuwar Sarkin Ruma, wanda ya rasu a lokacin da Sarkin ya ke wajen jihar.

A yayin ziyarar, Mai Martaba Sarkin Katsina ya shawarci ’yan Zuri’ar Danwaire da su ci gaba da kasancewa cikin hadin kai da kuma karfafa zumunci a tsakaninsu. Haka kuma ya ja hankalinsu da su ci gaba da raya kyawawan dabi’u da halaye nagari a cikin al’umma.

Da yake jawabi a madadin Zuri’ar, Gado-da-Masun Katsina, Hakimin Wagini, Alhaji Dikko Mu’azu, ya bayyana cewa sun zo ne domin mika sakon ta’aziyyarsu ga Mai Martaba bisa rasuwar Sarkin Ruma.

An gudanar da addu’o’i na musamman domin neman rahama ga marigayi da kuma neman karin lafiya da albarka ga Mai Martaba da daukacin al’ummar Jihar Katsina.

Tawagar ta kunshi Shugaban Karamar Hukumar Batsari, Alhaji Manir Mu’azu; Danwairen Katsina, Dr. Sada Salisu Rumah; da magada da ’yan uwa na marigayi Sarkin Ruma, Alhaji Tukur Mu’azu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Begins Selection of 34 Students for MBBS Scholarships in Russian Universities

The Katsina State Government has commenced the selection process for a special foreign scholarship programme that will sponsor 34 indigenous students to study Medicine (MBBS)...

FG Launches FreeTV Platform, Offers Nigerians Over 100 Subscription-Free Channels

The Federal Government has officially launched the FreeTV Direct-to-Home (DTH) platform, marking a major milestone in Nigeria's long-delayed Digital Switch-Over (DSO) programme and paving the...

Housing Minister Darma Inspects Digital Land Platform Ahead of Launch, Reaffirms Commitment to Modernising Land Administration

ABUJA — Minister of Housing and Urban Development, Engr. Muttaqha Rabe Darma, has inspected the Centralised Land Repository and Management System (CLRMS) ahead of its...

Most Popular