Fasaha Stream
LIVE Radio
Fasaha Stream
LIVE Radio

Zuri’ar Danwaire Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Mai Martaba Sarkin Katsina Kan Rasuwar Sarkin Ruma

-

Daga Sada Rumah

Zuri’ar Danwaire daga Karamar Hukumar Batsari sun kai ziyarar ta’aziyya ga Mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji (Dr.) Abdulmumin Kabir Usman, kan rasuwar marigayi Sarkin Ruma, Hakimin Batsari.

Ziyarar, wadda aka kai yau a Fadar Sarkin Katsina, ta kasance ne domin jajantawa Mai Martaba bisa rasuwar Sarkin Ruma, wanda ya rasu a lokacin da Sarkin ya ke wajen jihar.

A yayin ziyarar, Mai Martaba Sarkin Katsina ya shawarci ’yan Zuri’ar Danwaire da su ci gaba da kasancewa cikin hadin kai da kuma karfafa zumunci a tsakaninsu. Haka kuma ya ja hankalinsu da su ci gaba da raya kyawawan dabi’u da halaye nagari a cikin al’umma.

Da yake jawabi a madadin Zuri’ar, Gado-da-Masun Katsina, Hakimin Wagini, Alhaji Dikko Mu’azu, ya bayyana cewa sun zo ne domin mika sakon ta’aziyyarsu ga Mai Martaba bisa rasuwar Sarkin Ruma.

An gudanar da addu’o’i na musamman domin neman rahama ga marigayi da kuma neman karin lafiya da albarka ga Mai Martaba da daukacin al’ummar Jihar Katsina.

Tawagar ta kunshi Shugaban Karamar Hukumar Batsari, Alhaji Manir Mu’azu; Danwairen Katsina, Dr. Sada Salisu Rumah; da magada da ’yan uwa na marigayi Sarkin Ruma, Alhaji Tukur Mu’azu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Radda Moves to Upgrade NYSC Camp, Seeks More Doctors, Science Teachers for Katsina

Katsina State Governor, Malam Dikko Umaru Radda, has pledged to improve facilities at the National Youth Service Corps (NYSC) orientation camp in the state and...

Governor Radda Flags Off 90,000 Bags of Grains for Vulnerable Households Across Katsina

Katsina State Governor, Malam Dikko Umaru Radda, has flagged off the distribution of 90,000 bags of 100kg assorted grains to vulnerable households across the state’s...

A.B. Dabai Secures NEMA Relief Materials for Flood-Affected Farmers in Danja

The member representing Bakori–Danja Federal Constituency in the House of Representatives, Hon. Abdullahi Balarabe Dabai (A.B. Dabai), has distributed food relief materials to cabbage farmers...

Most Popular