Fasaha Stream
LIVE Radio
Fasaha Stream
LIVE Radio

Zuri’ar Danwaire Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Mai Martaba Sarkin Katsina Kan Rasuwar Sarkin Ruma

-

Daga Sada Rumah

Zuri’ar Danwaire daga Karamar Hukumar Batsari sun kai ziyarar ta’aziyya ga Mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji (Dr.) Abdulmumin Kabir Usman, kan rasuwar marigayi Sarkin Ruma, Hakimin Batsari.

Ziyarar, wadda aka kai yau a Fadar Sarkin Katsina, ta kasance ne domin jajantawa Mai Martaba bisa rasuwar Sarkin Ruma, wanda ya rasu a lokacin da Sarkin ya ke wajen jihar.

A yayin ziyarar, Mai Martaba Sarkin Katsina ya shawarci ’yan Zuri’ar Danwaire da su ci gaba da kasancewa cikin hadin kai da kuma karfafa zumunci a tsakaninsu. Haka kuma ya ja hankalinsu da su ci gaba da raya kyawawan dabi’u da halaye nagari a cikin al’umma.

Da yake jawabi a madadin Zuri’ar, Gado-da-Masun Katsina, Hakimin Wagini, Alhaji Dikko Mu’azu, ya bayyana cewa sun zo ne domin mika sakon ta’aziyyarsu ga Mai Martaba bisa rasuwar Sarkin Ruma.

An gudanar da addu’o’i na musamman domin neman rahama ga marigayi da kuma neman karin lafiya da albarka ga Mai Martaba da daukacin al’ummar Jihar Katsina.

Tawagar ta kunshi Shugaban Karamar Hukumar Batsari, Alhaji Manir Mu’azu; Danwairen Katsina, Dr. Sada Salisu Rumah; da magada da ’yan uwa na marigayi Sarkin Ruma, Alhaji Tukur Mu’azu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

NGF Chairman, Education Minister Commission Radda Model Secondary School in Katsina

KATSINA — Chairman of the Nigerian Governors’ Forum and Governor of Kwara State, Abdulrahman Abdulrazaq, has commissioned the multi-million naira Radda Model Secondary School in...

Katsina IGR Jumps to ₦3bn Monthly on Fiscal Reforms — Radda

KATSINA — Governor Dikko Umaru Radda says Katsina State’s monthly Internally Generated Revenue (IGR) has increased from about ₦400 million to ₦3 billion, following reforms...

Dandagoro Emerges NUJ Chairman in Katsina as Radda Congratulates New Executive

KATSINA — A new executive council of the Nigeria Union of Journalists has been inaugurated in Katsina, with Aminu Garba Dandagoro emerging as chairman. Aminu Garba...

Most Popular